fidelitybank

Rikicin Ukraine: Rasha ba za ta taɓa ƴan Najeriya ba a Ukraine – Alexei Shebarahin

Date:

Jakadan ƙasar Rasha a Najeriya, Alexei Shebarshin, ya tabbatar wa da gwamnatin tarayya cewa, Rasha ba za ta taɓa ƴan Najeriya ba a rikicin da ke ƙara yin tsanani tsakanin kasar Rasha da Ukraine.

Jaridar Punch ta rawaito cewa, Ministan harkokin kasashen waje, Geoffrey Onyeama, wanda ya samu damar ganawar sirri da jakadan ya shaida wa Shebarshin cewa, Najeriya kawar Rasha ce.

A cewar Onyeama, yayin tattaunawa da Shebarshin, ya sanar da shi cewa, Najeriya ba za ta lamunci cin zarafin ƙasa da ƙasa ba daga wata ƙasar da ke karkashin Majalisar Dinkin Duniya, ƙasar da ke da jakada a Najeriya.

Sai dai Jakadan ya ce, Rasha ba ta kai wa farar hula farmaki, kuma ba za su bari a cutar da Najeriya ba kuma sojojinsu za su tabbatar sun kula. Hasali ma ba sa kai farmakin bangaren farar hula.

“Wannan ne matsayar gwamnatin tarayya kuma muna da ‘yan Najeriya guda 5,600 a Ukraine, kuma hankalin mu a tashe yake, musamman ganin bama-baman da ake aunawa Rasha. Gwamnatin Najeriya ta na shirin zuwa ƙwaso ‘yan kasar”. In ji Onyeama.

A martanin Jakadan Rasha a Ukraine, ya ce, zai yi wa shelkwatar su magana, kuma alamu sun nuna cewa, suna da alaka mai kyau da Najeriya. Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp