fidelitybank

Rikicin Ukraine: Putin ba zai gana da ‘yan jaridu ba – Fadar Kremlin

Date:

Fadar Kremlin ta ce shugaban Rasha Vladimir Putin ba zai gudanar da taron manema labarai na karshen shekara ba a wannan shekara.

Gidan talabijin na Al Jazeera ya ba da rahoton cewar, mai magana da yawun fadar ta Kremlin, Dmitry Peskov, wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin, ya kuma lura cewa Shugaba Putin “yana magana akai-akai ga manema labarai, gami da ziyarar kasashen waje”.

Sai dai bai bayar da dalilin kin gudanar da taron manema labaran ba, wanda yakan dauki tsawon sa’o’i da dama ya na ganawa da ‘yan jaridu.

Masu lura da al’amuran yau da kullum, na kallon matakin a matsayin yakin da Rasha ke yi da Ukraine, wanda ya fara a watan Fabrairu.

Vladimir Putin, wanda ke kan karagar mulki tun shekara ta 2000, ya gudanar da taron manema labarai a cikin watan Disamba mafi yawan shekarun mulkinsa, lamarin da ya yi amfani da shi wajen haska hotonsa a gidan talabijin na kasar.

Dakatar da taron manema labarai na bana ya zama karo na farko a cikin shekaru goma da Putin ba zai gudanar da bikin na Disamba ba, wanda wata dama ce da ba kasafai ake samu ba ga manema labarai a wajen fadar Kremlin, ciki har da ‘yan jaridu na kasa da kasa, su yi wa shugaban Rasha tambayoyi kai tsaye.

Yakin da sojojin Rasha suka fara a kasar Ukraine ya zama abin tattaunawa a duniya, inda kasashen yammacin duniya ke kallonsa a matsayin wani mataki na tada kayar baya ga kasar Ukraine, don haka ya ci karo da jerin takunkumin karya tattalin arziki kan Rashan da ta mamaye kasar.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar Æ´ansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na É—aya daga cikin jhihohin da ake kaÉ—a...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp