fidelitybank

Rikicin Sudan: An kashe mutane fiye da 100 a yankin Darfur

Date:

Mummunan faɗa ya ɓarke a yankin Darfur na ƙasar Sudan, yayin da rahotonni ke cewa fiye da mutum 100 aka kashe a birnin El Geneina.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wakilan ɓangarorin da ke yaki da juna a ƙasar sun amince da kare fararen hula tare da barin kayan agaji kaiwa zuwa gare su.

Kungiyar kare haƙƙin bil-dama a yankin na Darfur ta ce babban limamin birnin El Geneina na daga cikin gwamman mutanen da suka mutu a rikicin da ya ɓarke a birnin.

Hotuna sun nuna yadda gine-gine suka lalace bayan da aka yi musu ruwan hare-hare da ta sama.

Ana zargin wata ƙungiyar Larabawa mai alaƙa da dakarun RSF da ƙaddamar da hare-hare kan gidaje a birnin.

Kusan shekara 20 bayan kisan kiyashin da aka tafka a yankin, har yanzu Darfur na ci gaba da fuskantar rikice-rikice.

Kungiyoyin bayar da agaji na ci gaba da janyewa yayin da cibiyoyin lafiya suka kasance a rufe, sakamakon faɗan da ya ɓarke a tsakanin sojojin ƙasar da dakarun RSF.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp