Mummunan faɗa ya ɓarke a yankin Darfur na ƙasar Sudan, yayin da rahotonni ke cewa fiye da mutum 100 aka kashe a birnin El Geneina.
Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wakilan ɓangarorin da ke yaki da juna a ƙasar sun amince da kare fararen hula tare da barin kayan agaji kaiwa zuwa gare su.
Kungiyar kare haƙƙin bil-dama a yankin na Darfur ta ce babban limamin birnin El Geneina na daga cikin gwamman mutanen da suka mutu a rikicin da ya ɓarke a birnin.
Hotuna sun nuna yadda gine-gine suka lalace bayan da aka yi musu ruwan hare-hare da ta sama.
Ana zargin wata ƙungiyar Larabawa mai alaƙa da dakarun RSF da ƙaddamar da hare-hare kan gidaje a birnin.
Kusan shekara 20 bayan kisan kiyashin da aka tafka a yankin, har yanzu Darfur na ci gaba da fuskantar rikice-rikice.
Kungiyoyin bayar da agaji na ci gaba da janyewa yayin da cibiyoyin lafiya suka kasance a rufe, sakamakon faɗan da ya ɓarke a tsakanin sojojin ƙasar da dakarun RSF.