Ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashen da ke maƙwabtaka da Ukraine, na ci gaba da karɓar ‘yan ƙasar da ke ficewa a dai-dai lokacin da yaƙi ke kara rincaɓewa.
Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ta ce, ta na aiki da ofisoshin jakadancin ƙasashen Ukraine da Poland da Rasha da Romania da kuma Hungary, domin tabbatar da ganin an mayar da su gida.
Bayanai sun ce, ɗaruruwan ‘yan Nijeriya ne suka tsallaka kan iyakar Ukraine, inda ake sa ran kwashe su zuwa birane mafiya aminci, kafin mayar da su Najeriya.
Romania ta kasance daya daga cikin kasashen da suka karbi ‘yan Najeriya da ke zaune a Ukraine.
Jakadiyar Najeriya a Romania, Safiya Nuhu,ta shaida wa BBC cewa, ya zuwa yanzu sun karbi ‘yan Najeriya 200 inda suke kyautata zaton za su samu fiye da haka.
Ta ce,” Bisa la’akari da cewa Najeriya tana da dalibai da dama a Ukraine, don haka mun san cewa dole a samu karin mutanen da za su shigo kuma mu a shirye muke mu karbe su don taimaka”.