fidelitybank

Rikicin Rasha da Ukraine: Kimanin ƴan Najeriya 200 sun shiga Romania daga Ukraine

Date:

Ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashen da ke maƙwabtaka da Ukraine, na ci gaba da karɓar ‘yan ƙasar da ke ficewa a dai-dai lokacin da yaƙi ke kara rincaɓewa.

Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ta ce, ta na aiki da ofisoshin jakadancin ƙasashen Ukraine da Poland da Rasha da Romania da kuma Hungary, domin tabbatar da ganin an mayar da su gida.

Bayanai sun ce, ɗaruruwan ‘yan Nijeriya ne suka tsallaka kan iyakar Ukraine, inda ake sa ran kwashe su zuwa birane mafiya aminci, kafin mayar da su Najeriya.

Romania ta kasance daya daga cikin kasashen da suka karbi ‘yan Najeriya da ke zaune a Ukraine.

Jakadiyar Najeriya a Romania, Safiya Nuhu,ta shaida wa BBC cewa, ya zuwa yanzu sun karbi ‘yan Najeriya 200 inda suke kyautata zaton za su samu fiye da haka.

Ta ce,” Bisa la’akari da cewa Najeriya tana da dalibai da dama a Ukraine, don haka mun san cewa dole a samu karin mutanen da za su shigo kuma mu a shirye muke mu karbe su don taimaka”.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp