Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas a ranar Lahadi, ya tarbi Rabiu Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), a Fatakwal, babban birnin jihar.
Tsohon gwamnan jihar Kano ya ziyarci jihar Rivers ne, domin kaddamar da titunan cikin gida na Mgbutanwo a karamar hukumar Emohua a ranar Litinin (yau).
Gwamna Wike a cikin ‘yan watannin da suka gabata, ya gayyaci ‘yan siyasa da dama daga jam’iyyun adawa zuwa gudanar da ayyukan da gwamnatinsa ta aiwatar.
Ku tuna cewa tsohon shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, APC Adams Oshiomhole ya je jihar a ranar Larabar da ta gabata don kaddamar da gadar sama ta 8 da ke kan titin Ada George, a karamar hukumar Obio-Akpor.
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi ya kuma kaddamar da gadar sama ta 9 a babbar mahadar Ikoku a ranar Alhamis.
Hakazalika, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da harabar makarantar Fatakwal na makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya a ranar Juma’a.