fidelitybank

Rikicin PDP: Ina kira ga magoya baya na ku kwantar da hankalin ku – Ortom

Date:

Biyo bayan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a jihar Benuwe, tsohon gwamna Samuel Ortom ya roki magoya bayan sa da su yi kasa-kasa da takubban su.

A kwanakin baya ne magoya bayan Ortom da na Sanata Gabriel Suswam suka yi artabu kan yadda ake tafiyar da tsarin jam’iyyar.

Jam’iyyar dai ta rabu gida biyu tare da rahotannin dakatarwar daga bangarori daban-daban.

Sai dai Ortom a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Terver Akase ya fitar a ranar Litinin ya bukaci duk masu tunawa da jam’iyyar da su yi kokarin wanzar da zaman lafiya da hadin kai a jihar.

Ortom ya jaddada cewa, a fagen siyasa, ra’ayoyi da mukamai daban-daban ba makawa ne, yana mai cewa bambance-bambancen sau da yawa yana taimakawa wajen zurfafa tsarin dimokuradiyya da kuma ba da gudummawa wajen wadatar da maganganu a tsakanin jam’iyyun siyasa.

Ya yi nuni da cewa, shi da Sanata Suswam suna da dadaddiyar abota da mutunta juna a matsayinsu na shugabanni a cikin jam’iyyar PDP, inda ya ce a kodayaushe za su nemo hanyoyin da za su magance duk wata rashin jituwar siyasa da ka iya tasowa.

Cif Ortom ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su jajirce tare da mai da hankali kan hadafi da muradun PDP, kamar yadda suka saba yi.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp