Gwamnonin uku na jam’iyyar APC, Gwamna Babajide Sanwoolu na jihar Legas, Gwamna Kayode Fayemi na Ekiti da Gwamna Rotimi Akeredolu, sun gana da gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike a Fatakwal a ranar Juma’a.
Wannan taro dai na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ya barke a jam’iyyar PDP, ta samu labarin cewa, gwamnonin uku jakadu ne da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu ya aika, domin neman goyon bayan Wike.
Ana kyautata zaton jam’iyya mai mulki da kuma Tinubu na kokarin yin amfani da karfin da ke tattare da rikicin jam’iyyar adawa ne, domin neman goyon bayan Wike a zaben shugaban kasa mai zuwa.
Idan dai za a iya tunawa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya ki amincewa da zabi Wike a matsayin abokin takararsa ko da an kafa kwamitin da zai zabi mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar ya zabi Gwamnan Ribas.
Hakan dai ya janyo rarrabuwar kawuna a jam’iyyar adawa. Da yake magana a taron, Fayemi ya ce;
“Za mu je Fatakwal ne domin ganawa da ‘ya’yan jam’iyyar APC a jihar, amma mun yanke shawarar yin amfani da damar wajen kai ziyarar ban girma ga abokin aikinmu gwamnan jihar.”
Gwamnan jihar Ribas dai ya ci gaba da adawa da dan takarar jam’iyyarsa Atiku, tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana Okowa a matsayin mataimakinsa.
Idan dai za a iya tunawa, a makon da ya gabata ne gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya yi tir da yadda jam’iyyar PDP da Atiku suka yi wa Wike markashiya, ya kuma shawarci dan takarar da ya tuhumi gwamnan.