fidelitybank

Rikicin PDP: Gwanoni 3 na APC sun ziyarci Wike

Date:

Gwamnonin uku na jam’iyyar APC, Gwamna Babajide Sanwoolu na jihar Legas, Gwamna Kayode Fayemi na Ekiti da Gwamna Rotimi Akeredolu, sun gana da gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike a Fatakwal a ranar Juma’a.

Wannan taro dai na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ya barke a jam’iyyar PDP, ta samu labarin cewa, gwamnonin uku jakadu ne da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu ya aika, domin neman goyon bayan Wike.

Ana kyautata zaton jam’iyya mai mulki da kuma Tinubu na kokarin yin amfani da karfin da ke tattare da rikicin jam’iyyar adawa ne, domin neman goyon bayan Wike a zaben shugaban kasa mai zuwa.

Idan dai za a iya tunawa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya ki amincewa da zabi Wike a matsayin abokin takararsa ko da an kafa kwamitin da zai zabi mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar ya zabi Gwamnan Ribas.

Hakan dai ya janyo rarrabuwar kawuna a jam’iyyar adawa. Da yake magana a taron, Fayemi ya ce;

“Za mu je Fatakwal ne domin ganawa da ‘ya’yan jam’iyyar APC a jihar, amma mun yanke shawarar yin amfani da damar wajen kai ziyarar ban girma ga abokin aikinmu gwamnan jihar.”

Gwamnan jihar Ribas dai ya ci gaba da adawa da dan takarar jam’iyyarsa Atiku, tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana Okowa a matsayin mataimakinsa.

Idan dai za a iya tunawa, a makon da ya gabata ne gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya yi tir da yadda jam’iyyar PDP da Atiku suka yi wa Wike markashiya, ya kuma shawarci dan takarar da ya tuhumi gwamnan.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp