fidelitybank

Rikicin PDP da APC: Mutum daya ya mutu a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta tabbatar da mutuwar wani mutum mai suna Abdullahi Isiyaku mai shekaru 37 a duniya, yayin da wasu da dama suka samu raunuka a rikicin da ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyar PDP da APC a karamar hukumar Maigatari.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Lawan Shiisu ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa DAILY POST.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da jam’iyyar adawa ta PDP ke gudanar da wani taro a Maigatari.

Shiisu ya bayyana cewa rikicin ya barke ne lokacin da magoya bayan jam’iyyar PDP suka isa sakatariyar jam’iyyar APC da ke Gangare Quarters inda suka kai wa wani Abdullahi Isiyaku hari.

Ya ce an garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa babban asibitin Gumel inda daga baya daya ya mutu a lokacin da ake jinya.

Shiisu ya ce, an kama mutane biyar da ake zargi da hannu a rikicin.

Ya ce an mayar da shari’ar zuwa ga SCID don yin bincike mai zurfi.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp