Isra’ila ta sake kashe wani kwamandan gwagwarmya na Falasɗinawa daga ƙungiyar Palestinian Islamic Jihad (PIJ), yayin da adadin waɗanda ta kashe a hare-haren Zirin Gaza ke ƙaruwa.
Yara ƙananana shida da mayaƙan PIJ da dama – ciki har da jagorori Khalid Mansour da Tayseer Jabari na cikin Falasɗinawa 32 da aka kashe zuwa yanzu.
Makaman roka da mortar kusan 600 ‘yan gwagwarmaya suka harba kan Isra’ila daga Gaza tun daga Juma’a, a cewar wani jami’in gwamnatin yankin.
Wannan ne tashin hankali mafi girma tsakanin ɓangarorin biyu tun wanda aka yi na kwana 11 a watan Mayun 2021, wanda ya yi sanadiyyar kashe Falasɗinawa fiye da 200 da kuma Isra’ilawa kusan 12.
Jami’an Isra’ilar na gargaɗin cewa hare-haren da take kaiwa za su ɗauki tsawon mako ɗaya.
A ranar Lahadi, makamin roka da Falasɗinawa ke harbawa sun kai Birnin Ƙudus a karon farko tun yaƙin 2021. In ji BBC.