fidelitybank

Rikicin Gaza da Yahudawa ka iya shanye shekarar 2024 – Isra’ila

Date:

Rundunar sojin Isra’ila ta ce, tana tsammanin rikici a Gaza zai ci gaba da gudana a tsawon shekara ta 2024.

A wani saƙon sabuwar shekara, mai magana da yawun rundunar tsaron Isra’ila Daniel Hagari ya ce an daidaita harkar tura dakarun soji don shirin tunkarar “faɗa na tsawon lokaci”.

Ya ce za a janye wasu dakaru – musamman ma sojojin wucin gadi – don ba su damar sake tattaruwa.

“Waɗannan gyare-gyare ana yin su ne don tabbatar da ganin an yi tsare-tsare da shirye-shirye da nufin ci gaba da yaƙi a shekara ta 2024,” in ji shi.

Ya ce wasu sojoji masu wucin gadi za bar Gaza “tun a wannan mako” don ba su damar “sake kintsawa gabanin wasu ayyuka da ke tafe”.

Mutum 21,978 – akasari mata da ƙananan yara ne – aka kashe a Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoba, a cewar ma’aikatar lafiya da ke ƙarƙashin ikon Hamas. Ta kuma an jikkata mutum 56,697 a Gaza a tsawon wannan lokaci.

Adadin ya haɗar da na mutum 156 da aka kashe da 246 da aka ji wa raunuka a tsawon sa’a 24 da ta wuce, ma’aikatar ta ƙra da cewa.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp