fidelitybank

Rikicin Fubara da Wike ya dauki dumi a jihar Rivers

Date:

Jami’an tsaron da ke gadin harabar majalisar dokokin jihar Rivers sun ƙulle ƙofar majalisar tare da hana gwamnan jihar Siminalayi Fubara shiga zauren majalisar.

Cikin wani bidiyo da sakataren yaɗa labaran gwamnan ya wallafa shafinsa na Facebook ya ce Fubara ya je majalisar ne domin gabatar da kasafin kuɗin jihar na 2025.

Rahotonni daga birnin Fatakwal sun ce tarin jami’an tsaron da aka jibge a harabar sun rufe ƙofar shiga majalisar a lokacin da gwamnan ya hallara tare da tawagarsa domin gabatar da kasafin.

Bayanai sun ambato jami’an tsaron na cewa sun yi hakan ne saboda ba a sanar da su labarin zuwan gwamnan a hukumance ba.

To sai dai Gwamna Fubara ya ce tuni ya aike wa kakakin majalisar, Martins Amaewhule wasikar sanar da shi zuwansa, kuma ya yi ƙoƙarin kiransa a waya tun ranar Talata.

A makonnin da suka gabata ne dai Kotun Ƙolin ƙasar ta yanke hukunci hana CBN bai wa jihar kason kuɗaɗenta daga tarayya saboda rashin gabatar da kasafin kuɗi a gaban halastacciyar majalisar dokokin jihar.

Haka kuma kotun ta yanke hukuncin maido da ƴanmajalisar jihar 27 da suka sauya sheƙa zuwa APC, tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar.

To sai dai a ranar 28 ga watan Fabrairu, Fubara ya sanar da yin aiki da hukuncin kotun tare da umartar hukumar zaɓen jihar ta shirya sabon zaɓen ƙananan hukumomin.

Tuni dai hukumar ta saka ranar 9 ga watan Agustan 2025 domin gudanar da sabon zaɓe.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp