fidelitybank

Rikicin cikin gida ne ya kayar da gwamnan Osun – APC

Date:

Shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa, Sanata Abdullahi Adamu, a ranar Talatar da ta gabata ya dora laifin rashin nasarar zaben gwamnan jihar Osun da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata kan rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar a matakin jihar.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Ademola Adeleke ne ya lashe zaben bayan ya samu kuri’u 403,371 inda ya kayar da gwamna mai ci Gboyega Oyetola wanda ya samu kuri’u 375,927 a zaben da aka gudanar a fadin kananan hukumomi 30 na jihar.

Da yake nasa jawabin, tsohon gwamnan jihar Nasarawa ya jaddada cewa jam’iyyar ta amince da shan kaye da gaskiya kuma ta koyi darasi mai kyau daga gare ta.

Sai dai ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam’iyyar APC ce za ta lashe zabe mai zuwa yayin da ya yi kira ga jam’iyyar adawa ta PDP da ta jira sakamakon babban zaben.

Ya ce, “Mun yi rashin nasara a gasar ba don ba za mu iya ba amma saboda rikicin ne ya haddasa shi. Mun yi gagarumin taron magoya baya kwanaki kadan kafin zaben a Osogbo. Mutum ba zai taba tsammanin za mu fadi zabe ba.

“Amma al’adar rayuwa ce ku rasa wani abu da kuke bukata sosai. Mun amince da shan kaye da imani kuma muna daukar darasi daga ciki.

“Kayewar Osun ko ta wace hanya ba ya nuna rashin nasararmu a babban zabe. Jiha daya kawai muka rasa daga cikin 22 da muke da su; ka ga har yanzu muna da karfi.

“Za mu zauna mu binciki kanmu. Dole ne mu tambayi kanmu abin da yake daidai da abin da ba daidai ba, me ke bukatar gyara,” inji shi.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp