Darakta Janar na kungiyar Gwamnonin na jam’iyar APC, Salihu Moh. Lukman ya yi murabus daga mukaminsa, sakamakon rikicin da ya biyo bayan babban taron jam’iyyar APC mai mulki da za ta gudanar a watan Fabrairu.
Vanguard ta rawaito cewa, murabus din nasa ya biyo bayan taron kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC a daren Lahadi, inda wasu kadan daga cikin gwamnonin suka bukaci a tsige shi.
An ce da yawa daga cikin gwamnonin sun yi fatali da bukatar suna masu cewa a bar tsohon shugaban PGF ya ci gaba da magana a matsayinsa na jigo a jam’iyyar.
Ko da yake Lukman bai mayar da martani ga manema labarai nan take ba, domin neman amsar sa, wani jami’in jam’iyyar ya ce “Shugaban PGF ya yi abin da ya dace ta hanyar yin abin da ya dace”.