fidelitybank

Rikicin APC: Bafarawa ya caccaki El-Rufa’i a kan Tinubu

Date:

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa, ya caccaki gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai kan kalamansa na cewa akwai shirin yin zagon kasa ga nasarar da ake sa ran dan takarar jam’iyyar APC, Bola Tinubu zai samu.

Naija News ta ruwaito cewa, El-Rufai, a wata hira da ya yi da BBC Hausa, ya yi ikirarin cewa akwai wasu abubuwa a Aso Rock da ke yiwa jam’iyya mai mulki zagon kasa da karancin kudin Naira a wani yunkuri na yin tasiri ga nasarar da jam’iyyar ta samu a zaben.

Da yake mayar da martani da manema labarai a Abuja ranar Saturda, Bafarawa ya shaida wa gwamnan Kaduna cewa babu wani yunkuri na yi wa jam’iyyar APC zagon kasa ko kuma mai rike da tutarsa, Bola Tinubu.

Jigon jam’iyyar PDP ya bukaci El-Rufai da ya daina nanata cewa dole ne Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa mai zuwa, yana mai jaddada cewa Arewa ba ta goyon bayan dan takarar APC.

A cewar Bafarawa, El-Rufai ko wani ba shi da hurumin dora dan takararsa a kan wasu mutanen Arewa.

Karanta Wannan: Zan cigaba da tallata Tinubu – Buhari

Ya ce: “Ya nanata cewa dole ne Tinubu ya ci zabe, ko mutane sun so ko ba su so, sun riga sun ci zabe. Wa ya gaya masa cewa duk yankin Arewa yana goyon bayan APC?

“Wannan ra’ayinsa ne kawai, idan haka ne, ba shi da hurumin dagewa kan Arewa saboda kowa yana da dan takararsa.

“Yadda yake yiwa Tinubu kamfen haka muke yiwa dan takararmu kamfen.”

“Za mu firgita su, za mu fahimtar da su cewa kasar nan ta kowa ce, ita ma Arewa.”

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp