fidelitybank

Rikicin APC: Bafarawa ya caccaki El-Rufa’i a kan Tinubu

Date:

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa, ya caccaki gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai kan kalamansa na cewa akwai shirin yin zagon kasa ga nasarar da ake sa ran dan takarar jam’iyyar APC, Bola Tinubu zai samu.

Naija News ta ruwaito cewa, El-Rufai, a wata hira da ya yi da BBC Hausa, ya yi ikirarin cewa akwai wasu abubuwa a Aso Rock da ke yiwa jam’iyya mai mulki zagon kasa da karancin kudin Naira a wani yunkuri na yin tasiri ga nasarar da jam’iyyar ta samu a zaben.

Da yake mayar da martani da manema labarai a Abuja ranar Saturda, Bafarawa ya shaida wa gwamnan Kaduna cewa babu wani yunkuri na yi wa jam’iyyar APC zagon kasa ko kuma mai rike da tutarsa, Bola Tinubu.

Jigon jam’iyyar PDP ya bukaci El-Rufai da ya daina nanata cewa dole ne Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa mai zuwa, yana mai jaddada cewa Arewa ba ta goyon bayan dan takarar APC.

A cewar Bafarawa, El-Rufai ko wani ba shi da hurumin dora dan takararsa a kan wasu mutanen Arewa.

Karanta Wannan: Zan cigaba da tallata Tinubu – Buhari

Ya ce: “Ya nanata cewa dole ne Tinubu ya ci zabe, ko mutane sun so ko ba su so, sun riga sun ci zabe. Wa ya gaya masa cewa duk yankin Arewa yana goyon bayan APC?

“Wannan ra’ayinsa ne kawai, idan haka ne, ba shi da hurumin dagewa kan Arewa saboda kowa yana da dan takararsa.

“Yadda yake yiwa Tinubu kamfen haka muke yiwa dan takararmu kamfen.”

“Za mu firgita su, za mu fahimtar da su cewa kasar nan ta kowa ce, ita ma Arewa.”

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp