fidelitybank

Rikicin APC a Kano: Sifeto-Janar na Ƴan Sanda ya yi sammacin ɓangarorin Ganduje da Shekarau

Date:

 

Sifeto-Janar na Ƴan Sanda, Usman Alkali, ya gaiyace ɓangarorin da ke rikici a jam’iya mai mulki ta APC a Jihar Kano.
A ƴan watannin da su ka gabata ne rikici ya ɓarke a APC a Kano, inda tuni jam’iyar ta dare gida biyu, lamarin da ya haifar da ɓangarori biyu a ƙarƙashin jagorancin Gwamna mai ci, Abdullahi Umar Ganduje da kuma tsohon gwamna, Sanata Ibrahim Shekarau.
A tuna cewa, ɓangaren Shekarau sun kai takardar ƙorafi zuwa ga ofishin Sifeto-Janar ɗin, in da su ke zargin tsarin Ganduje da kai hari kan ofishin Sanata Barau Jibrin a Kano.
Nan da nan suma ɓangaren Ganduje su kai kai ƙarar tsagin Shekarau gaban Sifeto-Janar ɗin a bisa zargin su Shekarau ɗin da tada zaune tsaye a jihar.
Waɗannan ƙorafe-ƙorafe ka iya zama dalilin da ya sanya Sifeto-Janar ɗin ya gaiyace su domin shawo kan matsalar.
Wakilin jaridar PlatinumPost ya gano cewa tuni wakilan ɓangarorin su ka isa shalkwatar ƴan sandan da ke gidan Louis Edet a Abuja yau Talata da safe.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp