fidelitybank

Rikicin APC a Kano: Sifeto-Janar na Ƴan Sanda ya yi sammacin ɓangarorin Ganduje da Shekarau

Date:

 

Sifeto-Janar na Ƴan Sanda, Usman Alkali, ya gaiyace ɓangarorin da ke rikici a jam’iya mai mulki ta APC a Jihar Kano.
A ƴan watannin da su ka gabata ne rikici ya ɓarke a APC a Kano, inda tuni jam’iyar ta dare gida biyu, lamarin da ya haifar da ɓangarori biyu a ƙarƙashin jagorancin Gwamna mai ci, Abdullahi Umar Ganduje da kuma tsohon gwamna, Sanata Ibrahim Shekarau.
A tuna cewa, ɓangaren Shekarau sun kai takardar ƙorafi zuwa ga ofishin Sifeto-Janar ɗin, in da su ke zargin tsarin Ganduje da kai hari kan ofishin Sanata Barau Jibrin a Kano.
Nan da nan suma ɓangaren Ganduje su kai kai ƙarar tsagin Shekarau gaban Sifeto-Janar ɗin a bisa zargin su Shekarau ɗin da tada zaune tsaye a jihar.
Waɗannan ƙorafe-ƙorafe ka iya zama dalilin da ya sanya Sifeto-Janar ɗin ya gaiyace su domin shawo kan matsalar.
Wakilin jaridar PlatinumPost ya gano cewa tuni wakilan ɓangarorin su ka isa shalkwatar ƴan sandan da ke gidan Louis Edet a Abuja yau Talata da safe.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp