fidelitybank

Rikicikin Fubara da Wike na kara kamari

Date:

Daga jihar Ribas kuwa, har yanzu rikicin siyasa na cigaba da ruruwa, yayin da Gwamna Siminalayi Fubara zai fuskanci karin kalubale fiye da rikicin da ke faruwa da ‘yan majalisar da ke goyon bayan tsagin Wike.

Yanzu haka kungiyar kananan hukumomin ta kasa ALGON reshen jihar Ribas, ta zargi gwamna Fubara da rike kudaden da aka ware wa kananan hukumomi 23 na jihar.

Wannan mataki a cewar kungiyar ta ALGON, ya kawo musu cikas wajen gudanar da ayyukansu.

Shuwagabannin sun yi ikirarin cewa abin da Gwamnan ya yi daidai ne da soke kananan hukumomi a jihar.

Sun kuma nuna goyon bayan kiran tsige gwamnan da shugaban kwamitin riko na jam’iyyar APC, Tony Okocha ya yi, wanda ya bukaci majalisar dokokin jihar karkashin jagorancin Martins Amaewhule ta fara yunkurin tsige gwamnan.

Da yake yiwa manema labarai jawabi Allwell Ihunda, shugaban ALGON na jihar kuma shugaban karamar hukumar Fatakwal ya ce Fubara ya ci gaba da rike kason kananan hukumomi 23 na jihar Ribas tun daga watan Afrilun 2024.

 

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp