fidelitybank

Rikici ya yi sanadiyar mutuwar mutane 2 da ƙona gidaje 20 a Filato

Date:

A wani harin da aka kai a jihar Filato, wasu ‘yan bindiga da ake zargin Fulani makiyaya ne a ranar Alhamis sun kashe mutane biyu da gidaje 20 a karamar hukumar Bassa.

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wasu sassan karamar hukumar a ‘yan kwanakin nan. A hare-haren an lalata gonaki da dama da amfanin gona.

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association (MACBAN) reshen jihar ta zargi ‘yan asalin jihar da sanya wa shanunsu guba, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar shanu 90.

Shugaban kungiyar ci gaban Irigwe na kasa (IDA), Prince Robert Ashi, a ranar Juma’a, ya bayyana cewa, an kashe mutane biyu a ranar Alhamis tare da kona gidaje 20 a wani samame da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton Fulani ne makiyaya suka kai a kauyen Laake da ke gundumar Kwall.

A cewarsa, ‘yan bindigan a yawansu, sun kai farmaki kauyen Laake da misalin karfe 9:00 na dare, kuma ya ci gaba da cin wuta, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu.

Ashi ya ce: “Mutanen kauyen lokacin da suke barci, ‘yan bindigar suka kai hari kauyen da misalin karfe 9:00 na dare. Sun kashe mutane biyu, sun kona gidaje ashirin tare da raunata mutane biyar. Abin takaicin shi ne irin wannan harin na iya faruwa a lokacin da jami’an tsaro ke kokarin dakile ayyukan kashe-kashe a kasar Irigwe.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Gabriel Ubah Ogaba, ya ce amma har zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoto bai samu labari ba, amma zai bincika.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp