fidelitybank

Rikici ya yi sanadiyar mutuwar mutane 2 da ƙona gidaje 20 a Filato

Date:

A wani harin da aka kai a jihar Filato, wasu ‘yan bindiga da ake zargin Fulani makiyaya ne a ranar Alhamis sun kashe mutane biyu da gidaje 20 a karamar hukumar Bassa.

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wasu sassan karamar hukumar a ‘yan kwanakin nan. A hare-haren an lalata gonaki da dama da amfanin gona.

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association (MACBAN) reshen jihar ta zargi ‘yan asalin jihar da sanya wa shanunsu guba, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar shanu 90.

Shugaban kungiyar ci gaban Irigwe na kasa (IDA), Prince Robert Ashi, a ranar Juma’a, ya bayyana cewa, an kashe mutane biyu a ranar Alhamis tare da kona gidaje 20 a wani samame da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton Fulani ne makiyaya suka kai a kauyen Laake da ke gundumar Kwall.

A cewarsa, ‘yan bindigan a yawansu, sun kai farmaki kauyen Laake da misalin karfe 9:00 na dare, kuma ya ci gaba da cin wuta, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu.

Ashi ya ce: “Mutanen kauyen lokacin da suke barci, ‘yan bindigar suka kai hari kauyen da misalin karfe 9:00 na dare. Sun kashe mutane biyu, sun kona gidaje ashirin tare da raunata mutane biyar. Abin takaicin shi ne irin wannan harin na iya faruwa a lokacin da jami’an tsaro ke kokarin dakile ayyukan kashe-kashe a kasar Irigwe.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Gabriel Ubah Ogaba, ya ce amma har zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoto bai samu labari ba, amma zai bincika.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp