fidelitybank

Rikici ya sake kunno kai cikin PDP a Kano

Date:

Wutar rikici ta ƙara ruruwa a PDPn jihar Kano duk da hukuncin kotu na baya-bayan nan da kuma matakin ɗaukaka ƙara daga ɗaya banagaren.

Lamarin ya faru ne bayan ɓangen Sadiq Wali wanda wata kotun tarayya ta ce ba shi ne ɗan takarar gwamnan ba, kuma ya ɗaukaka ƙara, daga baya ya ƙaddamar da kwamitin yaƙin neman zaɓensa a jihar.

Sai dai ɓangaren da kotu ta ce shi halastacce na Muhammad Abacha ya fito ya yi Alla-wadai da wannan mataki yana cewa nuna raini ne ga kotu.

Bayanan da BBC ta samu na cewa a wannan Litinin ɗin ne ake sa ran kwamitin yaƙin neman zaben da ɓangaren Sadiq Wali suka ƙaddamar zai fara zama domin tattauna yadda zai gudanar da aikinsa.

A makon jiya ne aka kafa kwamitin, al’amarin da ya ƙara tayar da kura.

Ɓangaren Muhammad Abacha sun ce ba su tare da wannan matakin kamar, yadda Barrister Ibrahim Isa Wangida, lauyan jam’iyyar PDP a Kano ya shaida wa BBC.

To sai dai bangaren Sadiq Wali wanda ya ƙaddamar da kwamtin ya ce, waɗanda suke sukar wannan matakin ba su fahimci yadda tsarin yake ba, a ta-bakin kakinsu Dakta Yusuf Bello Danbatta.

Masharhanta dai na ganin duk wannan rikici da taƙaddama, jam’iyyar ce ke yi wa kanta sakiyar da babu ruwa, dai-dai lokacin da hankulan sauran jam’iyyu suka karkata ga yaƙin neman zaɓe.

Jam’iyyar ta PDP da ke sahun manyan masu hamayya a Kano har yanzu kanta a rarrabe yake lamarin da ake ganin hakan ba zai yi mata kyau, kasa da wata biyu a gudanar da zabe.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp