fidelitybank

Rikici ya rincabe tsakanin Indiya da Pakistan

Date:

Yawan mutanen da suka mutu a hare-haren indiya da Pakistan na ƙaruwa, inda aka ruwaito cewa aƙalla mutum 26 sun mutu, 46 kuma sun jikkata a Pakistan bayan hare-haren sojojin Indiya.

A ɓangaren Indiya kuma, mutum 10 ne suka mutu yayin da 32 suka samu raunuka a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi sakamakon harin ramuwar gayya daga Pakistan.

Sojojin Indiya ne dai suka fara ƙaddamar da wani hari mai suna “Operation Sindoor” inda suka hari wurare tara da ke cikin Pakistan da kuma yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.

Wannan harin ya haifar da martani cikin gaggawa daga Pakistan, wanda ya janyo rikicin da ya fi kowanne tsanani cikin fiye da shekaru ashirin da suka gabata tsakanin ƙasashen biyu masu makaman nukiliya.

Shugabannin ƙasashen biyu na gudanar da taron gaggawa a ranar Laraba domin tattaunawa kan rikicin.

Harin da Indiya ta kai da kuma ramuwar gayya daga Pakistan na faruwa ne a daidai lokacin da ake fama da matsanancin tashin hankali, bayan wani hari da aka kai a watan da ya gabata kan masu yawon buɗe ido a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi – wanda New Delhi ta ɗora alhakin hakan a kan Islamabad, sai dai Pakistan ta musanta wani hannu a cikin harin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da safiyar Laraba, gwamnatin Indiya ta ce dakarunta sun kai harin ne kan “wuraren ‘yan ta’adda da ke cikin Pakistan da kuma yankin Jammu da Kashmir da Pakistan ke iko da shi, inda ake shiryaw da kuma kaddamar da hare-hare a kan Indiya.”

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp