fidelitybank

Rikici ya rincabe tsakanin Indiya da Pakistan

Date:

Yawan mutanen da suka mutu a hare-haren indiya da Pakistan na ƙaruwa, inda aka ruwaito cewa aƙalla mutum 26 sun mutu, 46 kuma sun jikkata a Pakistan bayan hare-haren sojojin Indiya.

A ɓangaren Indiya kuma, mutum 10 ne suka mutu yayin da 32 suka samu raunuka a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi sakamakon harin ramuwar gayya daga Pakistan.

Sojojin Indiya ne dai suka fara ƙaddamar da wani hari mai suna “Operation Sindoor” inda suka hari wurare tara da ke cikin Pakistan da kuma yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.

Wannan harin ya haifar da martani cikin gaggawa daga Pakistan, wanda ya janyo rikicin da ya fi kowanne tsanani cikin fiye da shekaru ashirin da suka gabata tsakanin ƙasashen biyu masu makaman nukiliya.

Shugabannin ƙasashen biyu na gudanar da taron gaggawa a ranar Laraba domin tattaunawa kan rikicin.

Harin da Indiya ta kai da kuma ramuwar gayya daga Pakistan na faruwa ne a daidai lokacin da ake fama da matsanancin tashin hankali, bayan wani hari da aka kai a watan da ya gabata kan masu yawon buɗe ido a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi – wanda New Delhi ta ɗora alhakin hakan a kan Islamabad, sai dai Pakistan ta musanta wani hannu a cikin harin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da safiyar Laraba, gwamnatin Indiya ta ce dakarunta sun kai harin ne kan “wuraren ‘yan ta’adda da ke cikin Pakistan da kuma yankin Jammu da Kashmir da Pakistan ke iko da shi, inda ake shiryaw da kuma kaddamar da hare-hare a kan Indiya.”

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp