Yawan mutanen da suka mutu a hare-haren indiya da Pakistan na ƙaruwa, inda aka ruwaito cewa aƙalla mutum 26 sun mutu, 46 kuma sun jikkata a Pakistan bayan hare-haren sojojin Indiya.
A ɓangaren Indiya kuma, mutum 10 ne suka mutu yayin da 32 suka samu raunuka a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi sakamakon harin ramuwar gayya daga Pakistan.
Sojojin Indiya ne dai suka fara ƙaddamar da wani hari mai suna “Operation Sindoor” inda suka hari wurare tara da ke cikin Pakistan da kuma yankin Kashmir da Pakistan ke iko da shi.
Wannan harin ya haifar da martani cikin gaggawa daga Pakistan, wanda ya janyo rikicin da ya fi kowanne tsanani cikin fiye da shekaru ashirin da suka gabata tsakanin ƙasashen biyu masu makaman nukiliya.
Shugabannin ƙasashen biyu na gudanar da taron gaggawa a ranar Laraba domin tattaunawa kan rikicin.
Harin da Indiya ta kai da kuma ramuwar gayya daga Pakistan na faruwa ne a daidai lokacin da ake fama da matsanancin tashin hankali, bayan wani hari da aka kai a watan da ya gabata kan masu yawon buɗe ido a yankin Kashmir da Indiya ke iko da shi – wanda New Delhi ta ɗora alhakin hakan a kan Islamabad, sai dai Pakistan ta musanta wani hannu a cikin harin.
A cikin wata sanarwa da ta fitar da safiyar Laraba, gwamnatin Indiya ta ce dakarunta sun kai harin ne kan “wuraren ‘yan ta’adda da ke cikin Pakistan da kuma yankin Jammu da Kashmir da Pakistan ke iko da shi, inda ake shiryaw da kuma kaddamar da hare-hare a kan Indiya.”