fidelitybank

Rikici ya lafa bayan Matasa sun yi wa DPO jina-jina da zargin kashe Matashi a Rano

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cewa an samu barkewar rikici a karamar hukumar Rano.

Lamarin ya tayar da hankalin mazauna yankin, wadanda ke ganin an hallaka baturen ‘yan sandan yankin, Baba Ali.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da rikicin a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ɗaya daga cikin mazauna garin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce: “Jiya akwai wani bawan Allah yana yawo a kan babur, sai aka kama shi aka kai shi wajen DPO, sai ya dake shi. Da ya ga dukan da ya yi masa, dukkan alamu ya jikkata sosai.” “Sai ya kai shi asibiti, daga bisani sai aka ce ya mutu da safe. Jama’ar gari sai suka tafi ofishin ‘yan sanda suna son su ɗauki fansa. Sai ‘yan sanda suka fara harba barkonon tsohuwa. Jama’a kuwa sai suka tayar da wuta. DPO kuma sai ya ɗauko bindiga ya harbe mutane biyu. Su kuma jama’a sai suka kona shi.”  Ya shaida wa manema labarai.

Rahotanni na nuni da cewa tuni aka sauya Baturen ‘yansandan yankin.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp