Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cewa an samu barkewar rikici a karamar hukumar Rano.
Lamarin ya tayar da hankalin mazauna yankin, wadanda ke ganin an hallaka baturen ‘yan sandan yankin, Baba Ali.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da rikicin a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Ɗaya daga cikin mazauna garin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce: “Jiya akwai wani bawan Allah yana yawo a kan babur, sai aka kama shi aka kai shi wajen DPO, sai ya dake shi. Da ya ga dukan da ya yi masa, dukkan alamu ya jikkata sosai.” “Sai ya kai shi asibiti, daga bisani sai aka ce ya mutu da safe. Jama’ar gari sai suka tafi ofishin ‘yan sanda suna son su ɗauki fansa. Sai ‘yan sanda suka fara harba barkonon tsohuwa. Jama’a kuwa sai suka tayar da wuta. DPO kuma sai ya ɗauko bindiga ya harbe mutane biyu. Su kuma jama’a sai suka kona shi.” Ya shaida wa manema labarai.
Rahotanni na nuni da cewa tuni aka sauya Baturen ‘yansandan yankin.