fidelitybank

Rikici ya lafa bayan Matasa sun yi wa DPO jina-jina da zargin kashe Matashi a Rano

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cewa an samu barkewar rikici a karamar hukumar Rano.

Lamarin ya tayar da hankalin mazauna yankin, wadanda ke ganin an hallaka baturen ‘yan sandan yankin, Baba Ali.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da rikicin a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ɗaya daga cikin mazauna garin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce: “Jiya akwai wani bawan Allah yana yawo a kan babur, sai aka kama shi aka kai shi wajen DPO, sai ya dake shi. Da ya ga dukan da ya yi masa, dukkan alamu ya jikkata sosai.” “Sai ya kai shi asibiti, daga bisani sai aka ce ya mutu da safe. Jama’ar gari sai suka tafi ofishin ‘yan sanda suna son su ɗauki fansa. Sai ‘yan sanda suka fara harba barkonon tsohuwa. Jama’a kuwa sai suka tayar da wuta. DPO kuma sai ya ɗauko bindiga ya harbe mutane biyu. Su kuma jama’a sai suka kona shi.”  Ya shaida wa manema labarai.

Rahotanni na nuni da cewa tuni aka sauya Baturen ‘yansandan yankin.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp