fidelitybank

Rigimar Wike da Atiku: Zamu ci gaba da kasancewa a PDP – Wike

Date:

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya bayyana kudurinsa na ci gaba da kasancewa a jam’iyyar PDP duk da raba gari da Atiku.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a daidai lokacin da ake ta kiraye-kirayen ya fice daga jam’iyyar saboda rikicin da ya kunno kai.

Wike ya bayyana haka ne a yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a jihar a fadar gwamnati da ke Fatakwal.

“Za mu yi yakin a cikin jam’iyyar. Ba mu kamar su, lokacin da a 2014 suka fita daga Eagle Square. Sun manta. Sun fita suka koma APC.

Shugaban Ribas ya ce wadanda ke gudu daga fadan mutane ne marasa karfi kuma ba zai yi haka ba.

Gwamnan ya yi nuni da cewa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya bayyana karara cewa dole ne a ware ofisoshin zabe da na jam’iyya.

“Kun dauki dan takarar shugaban kasa, kun dauki shugaban jam’iyya, kun dauki DG na yakin neman zabe. Muna magana ne kan siyasar jam’iyya.”

Wike ya ce dan takarar shugaban kasa, shugaban jam’iyyar da kuma DG na yakin neman zabe ne ke yanke hukunci.

“Kuna iya matsa wa shugaban BoT lamba ya yi murabus lokacin da wa’adin sa bai zo karshe ba. Amma ba za ku iya tursasa shugaban da ya yi murabus ba,” in ji shi.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp