fidelitybank

Real Madrid za ta kara da Chelsea a gasar Champions League

Date:

Kungiyar Real Madrid wadda ta zama gwarzuwa har sau 13 a gasar zakarun kungiyoyin Turai za ta kara da Chelsea da ta lashe gasar a bara.

Manchester city za ta kara da Atletico Madrid, yayin da Liverpool za ta barje gumi da Benfica sai kuma wasan Bayern munich da Villarreal.

Za a buka wasannin a ranar 5 da 6 ga watan Afrilu sai kuma 12 da 13 ga Afrilun wannan shekarar.

Za kuma a fafata a wasan kusa da na karshe a ranakun 26-27 sannan a buga na biyu a ranar 3-4 ga watan Mayu mai zuwa.

Za a buga wasan karshe na gasar a filin wasa na Stade de France da ke Faransa a ranar Asabar 28 ga watan Mayu, bayan dauke shi da ka yi daga St Petersburg bayan fara mamayar Rasha a Ukraine

Wannan na nufin Chelsea za ta sake haduwa da tsohon kocinta Carlo Ancelotti, wanda ya lashe gasar Premier sau biyu a shekara biyun da ya yi yana tafiyar da kungiyar tsakanin 2009 zuwa 2011.

Dan kasar Italiyan na daya daga cikin kociyoyin Itakiya da ya lashe Champions sau uku, lokacin da yake Real madrid a 2014, kungiyar da ya sake komawa kungiyar a bara da ya bar Everton.

Chelsea da Real madrid sun hadu a wasan kusa da na karshe a bara, yayin da kungiyar ta Thomas Tuchel ta cire Madrid da jimillar kwallaye 3-1 ta doke Manchester City a wasan karshe.

Atletico Madrid ta samu damar haduwa da Manchester biyu a wasa guda, bayan ta doke United da ci 2-1 a zagayen ‘yan 16.

Wannan ce fafatawar farko da za a yi tsakanin ATM da City wadda ta lallasa Sporting Lisbon da ci 5-0 a jimillar kwallaye da aka ci a wasanni biyu.

Liverpool kuma ta buga wasa da kungiyar Portugal Benfica 10 a gasar Turan, haduwar da aka yi ta karshe ita ce wadda aka yi 5-3 a wasan kusa da na karshe a 2010.

Jurgen Klopp na neman hada kofina hudu a wannan kakar, kuma tuni ya lashe kofin Carabao kuma ana fafatawa da shi a FA Cup da gasar Premier.

Wasa kusa da daf da na karshe

Chelsea da Real Madrid

Manchester City da Atletico Madrid

Villarreal da Bayern Munich

Benfica da Liverpool

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp