Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ya amince da naira 70,000 a matsayin mafi ƙanƙantar albashi ga ma’aikata jihar.
Cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce amincewar ta ƙunshi sake fasalin albashin ma’aikatan jihar ciki har da na ƙananan hukumomi da malaman makaranta.
Dikko Radda ya ce sabon albashin zai fara aiki daga watan Disamba mai kamawa.
”Ina miƙa godiya da jinjina ga ma’aikatan jihar Katsina bisa haƙuri da jajircewa da suka nuna, kuma ina kira a gare da ku ƙara jajircewa wajen aiki bisa gaskiya da riƙon amana…”, in ji gwamnan na Katsina.
A ranar Juma’a ne ƙungiyar NLC ta yi barazanar fara yajin aiki a wasu jihohin ƙasar ranar Litinin, ciki har da Katsina, saboda rashin amincewa da sabon tsarin albashin a jihohin.