fidelitybank

Rashin ‘yan Sanda na kawo mana cikas – IGP Olukayode

Date:

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya, Olukayode Egbetokun, ya ce rashin isassun ‘yan sanda, na kawo wa rundunarsu tarnaƙi wajen daƙile aikata laifuka a faɗin ƙasar.

Da yake gabatar muƙala – ga manyan jami’ai masu halartar kwas na 45 a cibiyar tsara manufofi da dabarun shugabanci ta Kuru a jihar Filato – Mista Egbetokun ya ce rundunar na buƙatar ƙarin ‘yan sanda 190,000 domin tabbatar da ayyukanta na tsaron rayuka da dukiyar al’umma a cikin gida.

Ya ce a yayin da Majalisar Dinkin Duniya ta tanadi cewa kamata ya yi ɗan sanda ɗaya ya kula da mutum 460, a Najeriya ɗan sanda ɗaya na kula da mutum 650 ne.

“Don haka rundunar ‘yan sanda na buƙatar ƙarin jami’ai 190,000 domin kai wa ga mizanin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tanada,” in ji shi.

Babban Sufeton ‘yan sandan ya ce idan ‘yan sanda ba su wadaci ƙasa ba, ba za a iya cimma burin manufofin gwamnati ba.

“Don haka, rashin wadatattun jami’ai, zai iya kawo cikas ga tabbatawar manufofin gwamnati,” in ji shi.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp