fidelitybank

Rashin Tsaro: ‘Yan Najeriya sama da miliyan 6 sun rasa muhalli – NCFRMI

Date:

Shugaban hukumar ta NCFRMI, Tijjani Aliyu, shi ya bayyana haka lokacin da ya kai wa gwamnan jihar Katisna Dikko Radda ziyara a ranar Juma’a.

Ya ce zuwa 2022, hukumar tana da mutum sama da miliyan uku waɗanda ambaliya da bala’o’i suka ɗaiɗaita, inda ya ce a yanzu an samu ƙaruwar mutanen da suka ɗaiɗaita da kashi 100.

“A yau zan iya cewa, muna da ƴan Najeriya da ba su kasa miliyan 6.1 waɗanda suka rasa gidajensu.

“Ya kamata a nemo hanyar koyawa waɗannan mutane sana’o’i da kuma ba su horo, saboda su dogara da kansu nan gaba, domin gwamnati ba za iya ci gaba da kula da dukkansu ba,” in ji Aliyu.

Ya ƙara da cewa hukumar tana yunkurin kafa cibiyoyi guda uku na koyon sana’o’i a faɗin arewa maso gabas.

Ya ce ya kai ziyarar ce domin raba abinci ga mutane sama da 700 waɗanda aka ɗaiɗaita a jihar ta Katsina.

Ya kuma ce sun horar da mutum 120, da kuma bai wa iyayensu da suka kai 70 kayakin yin sana’o’i domin kyautata rayuwarsu.

Har ila yau, ya ce sun gina gidaje a yankunan da sansanonin ƴan gudun hijira suke, musamman ga waɗanda ba su da ra’ayin komawa garuruwansu na asali.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp