Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa rashin tallafin agaji zai jefa sama mutum miliyan guda a yankin arewa maso gabashin Najeriya cikin barazanar Boko Haram.
WFP ta ce kuɗinta sun ƙare don haka ba za ta iya ci gaba da tallafa wa mutanen da suka tsere wa rikicin Boko Haram ba.
Ta yi fargabar cewa hakan zai tilatas wa mutane shiga ƙungiyar ta Boko Haram.
Kungiyar agaji ta likitocin MSF ta ce rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara sama da 600 a yankin a wannan shekara.