fidelitybank

Rashin shaidu 3 ya hana Abba buɗe kariyar sa a kotun zaɓe

Date:

Rashin halartan shaidu uku a ranar Juma’a ya hana Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) bude kariyarsa a kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kano.

APC na kalubalantar INEC kan ayyana dan takarar jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Wadanda suka amsa karar a gaban kotun sun hada da INEC, Yusuf da NNPP.

Da aka kira karar, Lauyan Yusuf, Mista Eyitayo Fatigun SAN, ya shaida wa kotun cewa shaidu ukun da suka gayyata ba su halarta ba.

“Muna ba da hakuri saboda shaidu ukun sun samu matsalar jirgin da zai tashi zuwa Kano daga Abuja. Muna neman a dage zaman,” in ji Fatigun

Lauyan INEC, Emmanuel Osayomi da Lauyan NNPP, John Olusola SAN, ba su yi adawa ba.

Shi ma lauyan wanda ya shigar da kara, Offiong Offiong SAN, bai yi adawa da bukatar dage shari’ar da wanda ake kara na biyu ya yi ba.

NAN ta ruwaito APC a ranar 15 ga watan Yuli, ta rufe karar ta, bayan ta kira shaidu 32, yayin da INEC ta rufe karar ta a ranar 21 ga watan Yuli.

Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay ya dage sauraron karar har zuwa ranar Asabar domin jam’iyyar NNPP ta bude karar.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp