Rashin halartan shaidu uku a ranar Juma’a ya hana Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) bude kariyarsa a kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kano.
APC na kalubalantar INEC kan ayyana dan takarar jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.
Wadanda suka amsa karar a gaban kotun sun hada da INEC, Yusuf da NNPP.
Da aka kira karar, Lauyan Yusuf, Mista Eyitayo Fatigun SAN, ya shaida wa kotun cewa shaidu ukun da suka gayyata ba su halarta ba.
“Muna ba da hakuri saboda shaidu ukun sun samu matsalar jirgin da zai tashi zuwa Kano daga Abuja. Muna neman a dage zaman,” in ji Fatigun
Lauyan INEC, Emmanuel Osayomi da Lauyan NNPP, John Olusola SAN, ba su yi adawa ba.
Shi ma lauyan wanda ya shigar da kara, Offiong Offiong SAN, bai yi adawa da bukatar dage shari’ar da wanda ake kara na biyu ya yi ba.
NAN ta ruwaito APC a ranar 15 ga watan Yuli, ta rufe karar ta, bayan ta kira shaidu 32, yayin da INEC ta rufe karar ta a ranar 21 ga watan Yuli.
Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay ya dage sauraron karar har zuwa ranar Asabar domin jam’iyyar NNPP ta bude karar.