fidelitybank

Rashin ciwon kai ne ga ƴan Najeriya su biya 575,000 domin tafiya yaƙi Ukraine – CISLAC

Date:

Ƙungiyoyin farar hula a Najeriya ciki harda CISLAC sun yi alla-wadai da matakin da ƙasar Ukraine ta ɗauka na kiran ƴan Najeriya da Afrika su taimaka mata da mutane, domin yaƙar Rasha.

Shugaban kungiyar CISLAC, Awwal Musa Rafsanjani, a tattaunawarsa da BBC cikin yanayi na nuna takaci ya ce, sam matakin bai dace ba.

Ya ce, ”Wannan kira da Ukraine ta yi wa kasashen Afrika, domin shiga yakin da ba su ji ba, ba su gani ba. Sam wannan bai dace ba, abin takaicin ma shi ne kafin ka je ka kai kan ka halaka sai ka biya dala 1,000 idan aka sauya zuwa kudin Najeriya ana maganar Naira 575,000.

“Ina ganin wannan rashin sanin ciwon kai ne ga ‘yan Najeriya, kuma gwamnati na da laifi wajen rashin fitowa ta nunawa ‘yan kasa illar da ke cikin wannan kasada.

“Ya dace ma’aikatar harkokin waje ta fito ta yi bayani dalla-dalla da gargadin ‘yan Najeriya kar su sanya kan su cikin abin da babu ruwansu a ciki, rigimar da ba ta shafe su ba, babu kuma wani alfanu da za su samu idan sun tsoma baki a ciki, abin ba zai amfani kasarsu da ma Afirka baki daya ba,” in ji Rafsanjani.

Ita ma ƙasar Senegal ta yi watsi da wannan umarni na Ukraine cewa, ya saɓa wa dokar ƙasar ta, sai dai kuma tuni mutane 36 a ƙasar su ka nuna sha’awar taimaka wa Ukraine, yayin da a Najeriya matasa sama da 100 su ka miƙa sunan su da adireshi da email a ofishin jakadancin Ukraine

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp