fidelitybank

Rashin cikakkun jami’an tsaro ya sa aka sace daliban Kuriga – Gwamnan Kaduna

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya ce babu isassun jami’an tsaro a yankunan da ke fama da hare-hare a jihar, lamarin da ya ce shi ne babban dalilin karuwar garkuwa da mutane a yankunan.

Gwamnan ya shaida wa BBC cewa kusan daliban makarantar Kuriga da aka sace 28 ne suka kubuta daga hannaun ‘yan bindigar da suka sace su.

Tuni dai sojojin Najeriye karkashin kulawar babban hafsan sojin kasa ke ci gaba da neman sauran yaran tare da hadin gwiwar ‘yan sanda da mafarauta a dazukan Kaduna da jihohin Zamfara da Katsina masu makwabtaka.

Su ma a nasu bangaren iyayen yaran da aka sacen sun kafa kungiyoyin ‘yan sa kai tare da neman agajin gaururuwan da ke makwabtaka da Kuriga ko za su samu labarin inda ‘ya’yan nasu suke.

Nan gaba a yau ne ake sa ran mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima zai kai ziyara jihar don ganawa da gwamnan, bisa umarnin shugaban kasa na kubutar da yaran.

Ana ci gaba da samun karuwar fargaba daga bangaren iyayen yara a yankin arewacin Najeriya, kan tsaron lafiyarsu a makarantun.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp