Wasu fusatattun mutane mazauna yankin Birnin Kudu a jihar Jigawa, sun kai wa tawagar dan majalisar su farmaki.
Rahotanni daga yankin na nuni da cewar, jama’ar, dan majalisa, Magaji Da’u, ya gaza yi musu wakilci nagari kuma ya zo ne yanzu yayin da zabe ke gabatowa.
Jama’ar sun caccaki tare da sukar dan majalisar tare da rufe hanyar da zai wuce, lamarin da ya janyo arangama tsakanin magoya bayansa da jama’ar.
Premiumtimes ta rawaito cewa, al’ummar yankin sun rufe hanyar da dan majalisar zai bi ya tafi yankin Kukuma, domin halartar wani taron siyasa, lamarin da ya sanya mazauna yankin su ka rinka zage-zage tare da maganganu marasa dadi, inda suke zargin dan majalisar da rashin wakilci nagari kuma da yin watsi da wadanda ya ke wakilta har sai yanzu da ya bayyana, saboda zaben 2023 ya na gabatowa.