fidelitybank

Rasha za ta girƙe makamin nukiliya a Belarus – Putin

Date:

Shugaban ƙasar Rasha Vladimir Putin ya ce ƙasarsa za ta girke makaman nukiliya a maƙabciyarta Belarus.

Kafofin yaɗa labaran Rasha sun ruwaito Mista Putin na cewa matakin ba zai saɓa wa yarjejeniyar ƙasa-da-ƙasa ta taƙaita yaɗuwar makaman nukiliyar ba, kamar yadda Amurka ta girke nata makaman a nahiyar Turai.

Shugaba Putin ya ce Rasha ba za ta mayar da ikon sarrafa makaman zuwa Belarus ɗin ba.

To sai dai Amurka ta bayyana damuwarta game da matakin, tana mai cewa ba ta ga dalilin yin hakan ba, a cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin tsaron ƙasar ta fitar.

Amurkan ta ce a shirye take wajen kare tsaron ƙasashen ƙungiyar tsaro ta NATO.

Ƙasar Belarus dai ta haɗa iyaka da Ukraine, da kuma ƙasashen Polan da Lithuania da Latvia, waɗanda mambobin NATO ne.

Wannan shi ne karon farko tun shekarun 1990, da Rasha za ta girke makamin nukiliyarta a wata ƙasar.

Bayan wargajewar tarayyar Soviet a shekarar 1991, duka makaman da ke ƙasashen Ukraine, da Belarus da kuma Kazakhstan – waɗanda duka suka samu ‘yancin gashin kai – an mayar da su zuwa Rasha a shekarar 1996.

Belarus ta kasance babbar ƙawar Rasha da ke goyon bayan mamayar da Rasha ke yi wa Ukraine. In ji BBC.

A wani jawabi da ya yi wa ‘yan ƙasar ta talbijin ranar Asabar shugaba Putin ya ce shugaban Belarus Alexander Lukashenko, ya daɗe yana kiran Rasha da ta girke makaman nukiliyarta a ƙasarsa.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp