fidelitybank

Rasha za ta baiwa Najeriya jiragen yaƙi 12

Date:

Rasha na son kammala samar da jiragen yaƙi masu saukar ungulu na Mi-35 guda goma sha biyu ga Najeriya, kamar yadda wani jami’i ya shaida wa kamfanin dillancin labaran ƙasar, Rian, a wajen taron Rasha da Afirka da ke gudana a birnin St Petersburg.

Dmitry Shugaev, shugaban ma’aikatar tarayya ta Rasha kan fasahar aikin soji, ya ce yarjejeniyar sojan ita ce ta taimaka wa Najeriya wajen yaƙi da barazanar kungiyoyin ƴan ta’adda da kuma shigar da ƙasar cikin ayyukan wanzar da zaman lafiya.

He did not specify the number of the combat aircrafts delivered so far or when the delivery will be completed but said “the partners are interested in its completion, we continue to work in this direction”.

Bai bayyana adadin jiragen yaƙin da aka kawo ba zuwa yanzu ko kuma lokacin da za a kammala kawo sauran jiragen ba, amma ya ce “Ƙasashen na sha’awar kammala jigilar jiragen, muna ci gaba da yin aiki ta wannan fuskar.”

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya ce Najeriya za ta haɗa gwiwa da ƙasar Rasha domin farfaɗo da kamfanin sarrafa aluminium.

Yarjejeniyar dai na daga cikin yarjejeniyoyin da ake sa ran za a ƙulla a yayin taron, wanda shi ne irinsa na biyu bayan da aka yi na farko a shekarar 2019 a birnin Sochi.

Mista Shettima dai yana halartar taron ne tare da wasu shugabannin ƙasashen Afirka.

Tuni dai Rasha ta yi alkawarin samar da hatsi kyauta ga Zimbabwe da wasu ƙasashen Afrika biyar. A cewar rahoton BBC.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp