fidelitybank

Rasha ta yi nuni da Iran da Isra’ila su yi taka-tsantsan

Date:

Rasha ta yi kira ga dukkan ɓangarori da su yi taka-tsantsan da kuma nuna damuwarsu kan yaɗuwar rikici bayan da Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka zuwa Isra’ila cikin dare.

Ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta bayyana cikin wata sanarwa da ta fitar cewa “Mun dogara ga ƙasashen yankin wajen ganin sun magance matsalolin da ake fama da su ta hanyar siyasa da diflomasiyya.”

Moscow ta kara da cewa sau da dama ta yi gargaɗin cewa kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kasa mayar da martani mai kyau game da harin da aka kai kan karamin ofishin jakadancin Iran a ƙasar Siriya, wanda ya yi sanadin mutuwar jami’ai bakwai na dakarun juyin-juya halin Iran da suka haɗa da manyan kwamandoji.

Hakan na zuwa ne bayan da Amurka da Birtaniya da Faransa suka nuna adawa da sanarwar da Rasha ta rubuta wa kwamitin sulhu na MDD wanda zai yi Alla-wadai da harin da aka kai harabar ofishin jakadancin Iran a Syria.

Iran ta zargi Isra’ila da kai wannan harin, amma Isra’ilar ta ce ba ta cewa uffan kan rahotannin ƙasashen waje.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp