fidelitybank

Rasha ta yi nuni da Iran da Isra’ila su yi taka-tsantsan

Date:

Rasha ta yi kira ga dukkan ɓangarori da su yi taka-tsantsan da kuma nuna damuwarsu kan yaɗuwar rikici bayan da Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka zuwa Isra’ila cikin dare.

Ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta bayyana cikin wata sanarwa da ta fitar cewa “Mun dogara ga ƙasashen yankin wajen ganin sun magance matsalolin da ake fama da su ta hanyar siyasa da diflomasiyya.”

Moscow ta kara da cewa sau da dama ta yi gargaɗin cewa kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kasa mayar da martani mai kyau game da harin da aka kai kan karamin ofishin jakadancin Iran a ƙasar Siriya, wanda ya yi sanadin mutuwar jami’ai bakwai na dakarun juyin-juya halin Iran da suka haɗa da manyan kwamandoji.

Hakan na zuwa ne bayan da Amurka da Birtaniya da Faransa suka nuna adawa da sanarwar da Rasha ta rubuta wa kwamitin sulhu na MDD wanda zai yi Alla-wadai da harin da aka kai harabar ofishin jakadancin Iran a Syria.

Iran ta zargi Isra’ila da kai wannan harin, amma Isra’ilar ta ce ba ta cewa uffan kan rahotannin ƙasashen waje.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp