Ma’aikatar tsaron Rasha ta sanar da cewa, ta bude wasu hanyoyin jin kai, domin fararen hular Ukraine su fice daga garuruwan Cherhihiv da Sumy da Kharkiv da Mariupol da kuma Kyiv babban birnin kasar.
Yunkurin da a ke yi a kwanakin baya sun gamu da cikas, inda aka rika bude wa fararen hular wuta.
Kamfanin dillancin labarai na Interfax na kasar Rasha ya rawaito cewa, sojojin Rasha sun daina bude wuta tun karfe 7 agogon GMT, wato karfe bakwai ke nan agogon Najeriya, Kamaru, Nijar da Chadi.