Shugaba Volodymyr Zelensky na Ukraine ya yi gargaɗin cewa, Rasha na sake girke ƙarin dakarun ydomin kai sabbin hare-hare gabashin kasar.
Ya ce gwamnatin Rasha ta ƙara tura wasu dakaru yankin Kharkiv da ke arewa maso gabashi a ƙoƙarin sake matsa kaimi a Donbass.
A ranar Asabar dakarun Ukraine suka ce sun kai hari kan wani sansanin Rasha da ke kusa da Kharkiv, da sake karɓe ikon wasu yankunan.
Sai dai sun ce Rasha na c igaba da mayar da hankali wajen sake gina ƙarin sojoji kusa da iyaka da kuma garin Izium.
Jami’an a yankin Luhansk sun ce luguden wutar Rasha na ƙaruwa a kullum.
Rahotanni na cewa hare-haren Rasha a gabashi na tsanani yayin da Shugaban yankin Luhansk ya ce yana tunanin Rasha na shirin kai hari mafi girma a ranar 9 ga watan Mayu – ranar da bisa al’ada ta saba bikin murnar nasarar da ta samu galabar Jamus a yankin duniya na Biyu