Ma’aikatar tsaro ta Rasha ta ce, dakarunta sun ƙwace iko da garin Kherson da ke kudancin Ukraine.
Idan ta tabbata, zai zama gari mafi girma da Rasha ta karɓe iko da shi tun bayan fara kai hare-hare ranar Alhamis da ta wuce.
Tun cikin dare rahotanni suka ruwaito cewa an ga dakarun Rasha a titunan birnin, inda magajin garin ke cewa an ƙwace filin jirgin ƙasa da kuma tashar jiragen ruwa.