Shugaban ƙawancen tsaro na NATO ya ce hukumomin leƙen asiri na kasashen Yammacin duniya sun tabbatar da cewa, Rasha ba ta cika alƙawuran da ta dauka na rage yawan hare-haren da dakarunta ke kaiwa a yankin birnin Kyiv da Arewacin Ukraine ba.
Jens Stoltenberg ya ce, sojojin Rasha ba su janye ba, sai dai ana sauya musu wuri ne domin su kara shirin kai wasu hare-haren a yankin Donbas da ke gabashin kasar.
Mista Stoltenberg ya kuma ce, Rasha na ci gaba da harin da ta ke kai wa biranen Kyiv da sauran birane, kuma ya ce Rasha ta ci gaba da yin karyar cewa za ta janye daga yankunan.
Wata mazauniyar birnin Chernihiv ta ce: “Ta yaya za su ce sun rage yawan sojojinsu? Muna ci gaba da jin karar bama-bamai. Ba ma iya barci, mun fuskanci tashin hankali cikin kwanaki biyun da suka gabata.”