Wata kungiyar agaji ta ce, Rasha ta kama wasu ma’aikatan agaji biyu ‘yan Birtaniya.
Kungiyar agajin mai suna, Presidium Network ta ce, an tsare mutanen ne a wani shingen da Rasha ta kafa kusa da birnin Zaporizhzhia a kudancin Ukraine tun ranar Litinin.
Daya daga cikin jagororin kungiyar ta Presidium Dominic Byrne, ya ce ma’aikatan na kokarin ceto wasu ‘yan gida daya ne da yakin ya rutsa da su.
“Sun sami wuce wani wurin bincike da sojojin Ukraine suka kafa a hanyar su ta zuwa kudancin yankin sai dai zuwa ranar Litinin ba mu kara ji daga garesu ba,” kamar yadda ya sanar da wani shirin talabijin na BBC Breakfast.
Ya ce mutanen da ke jiran su ceto su, sun rinka samun sakonni daga wayar ‘yan Birtaniyan biyu, kuma bayan sa’o’i biyu sai sojojin Rasha suka kutsa cikin gidan, sun tambayi alakarsu da ma’aikatan agajin, a matsayin ‘yan leken asiri ne.
Ma’aikatar harkokin wajen Birtaniya ta c,e tana kokarin sanin halin da suke ciki.