Rasha ta sanar da ficewa daga yarjejeniyar da ta shiga da ƙasashen duniya wadda ta bai wa Ukraine damar fita da kayan abinci ta Baƙin Teku.
Ta ce ta ɗauki matakin ne sakamakon harin da ta zargi Ukraine ɗin da kaiwa kan jirgane ruwanta da ke yankin Crimea da Rashar ta mamaye a 2014.
Cikin fushi, Amurka ta mayar da martani kan matakin.
“Wannan mataki ne mai ɗaga hankali kuma zai iya jawo ƙaruwar yunwa haka kuma kuma ba su da wata hujja da suke da ita da za su ɗauki matakin,” in ji Shugaba Joe Biden.
Haka kuma Sakataren harkokin waje na kasar Anthony Blinken shi ma ya zargi Rasha da mayar da abinci tamkar wani makami.
Tun da farko dai Rasha ta ce za ta janye daga wannan yarjejeinyar ne sakamakon harin jirage marasa matuka da aka kai wa jiragen ruwanta a yankin Crimea.