fidelitybank

Rasha ta bayar da tabbacin tsare lafiyar ƴan Najeriya a Ukraine da ƙasar ta

Date:

Hukumomin kasar Rasha sun tabbatar wa ‘yan Najeriya da ke cikin ƙasar cewa, za a ci gaba da ba su tallafin da suka dace, domin tabbatar da tsaron lafiyarsu da jin dadinsu.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Moscow na kasar Rasha ya fitar ranar Juma’a a gefen taron da jami’an kasashen biyu suka yi.

Ganawar ta kasance tsakanin, Farfesa Abdullahi Shehu, jakadan Najeriya mai cikakken iko a kasar Rasha tare da amincewar kasar Belarus, da Mikhail Bogdanov, wakilin Tarayyar Rasha a Gabas ta Tsakiya da Afirka.

Bogdanov, wanda kuma shi ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha, ya ba da tabbacin a ganawar da suka yi da Shehu a ofishinsa.

Sanarwar ta ce: Bogdanov ya sanar da Shehu game da shirye-shiryen dabaru da Rasha ta yi, domin taimakawa wajen kwashe daliban Najeriya da suka makale a Kherson, Ukraine.

Ya tabbatar wa jakadan cewa, gwamnatin Rasha za ta ba da taimakon da ya dace, domin tabbatar da tsaro da jin dadin ‘yan Najeriya a Tarayyar Rasha.

A yayin tattaunawar ta su, an tattauna halin da ake ciki a Ukraine, da kuma batutuwa da dama da suka shafi ci gaban dangantakar abokantaka tsakanin Rasha da Najeriya a nan gaba.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp