fidelitybank

Rasha ta bayar da tabbacin tsare lafiyar ƴan Najeriya a Ukraine da ƙasar ta

Date:

Hukumomin kasar Rasha sun tabbatar wa ‘yan Najeriya da ke cikin ƙasar cewa, za a ci gaba da ba su tallafin da suka dace, domin tabbatar da tsaron lafiyarsu da jin dadinsu.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Moscow na kasar Rasha ya fitar ranar Juma’a a gefen taron da jami’an kasashen biyu suka yi.

Ganawar ta kasance tsakanin, Farfesa Abdullahi Shehu, jakadan Najeriya mai cikakken iko a kasar Rasha tare da amincewar kasar Belarus, da Mikhail Bogdanov, wakilin Tarayyar Rasha a Gabas ta Tsakiya da Afirka.

Bogdanov, wanda kuma shi ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha, ya ba da tabbacin a ganawar da suka yi da Shehu a ofishinsa.

Sanarwar ta ce: Bogdanov ya sanar da Shehu game da shirye-shiryen dabaru da Rasha ta yi, domin taimakawa wajen kwashe daliban Najeriya da suka makale a Kherson, Ukraine.

Ya tabbatar wa jakadan cewa, gwamnatin Rasha za ta ba da taimakon da ya dace, domin tabbatar da tsaro da jin dadin ‘yan Najeriya a Tarayyar Rasha.

A yayin tattaunawar ta su, an tattauna halin da ake ciki a Ukraine, da kuma batutuwa da dama da suka shafi ci gaban dangantakar abokantaka tsakanin Rasha da Najeriya a nan gaba.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp