fidelitybank

Rasha ta bayar da tabbacin tsare lafiyar ƴan Najeriya a Ukraine da ƙasar ta

Date:

Hukumomin kasar Rasha sun tabbatar wa ‘yan Najeriya da ke cikin ƙasar cewa, za a ci gaba da ba su tallafin da suka dace, domin tabbatar da tsaron lafiyarsu da jin dadinsu.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Moscow na kasar Rasha ya fitar ranar Juma’a a gefen taron da jami’an kasashen biyu suka yi.

Ganawar ta kasance tsakanin, Farfesa Abdullahi Shehu, jakadan Najeriya mai cikakken iko a kasar Rasha tare da amincewar kasar Belarus, da Mikhail Bogdanov, wakilin Tarayyar Rasha a Gabas ta Tsakiya da Afirka.

Bogdanov, wanda kuma shi ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha, ya ba da tabbacin a ganawar da suka yi da Shehu a ofishinsa.

Sanarwar ta ce: Bogdanov ya sanar da Shehu game da shirye-shiryen dabaru da Rasha ta yi, domin taimakawa wajen kwashe daliban Najeriya da suka makale a Kherson, Ukraine.

Ya tabbatar wa jakadan cewa, gwamnatin Rasha za ta ba da taimakon da ya dace, domin tabbatar da tsaro da jin dadin ‘yan Najeriya a Tarayyar Rasha.

A yayin tattaunawar ta su, an tattauna halin da ake ciki a Ukraine, da kuma batutuwa da dama da suka shafi ci gaban dangantakar abokantaka tsakanin Rasha da Najeriya a nan gaba.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp