Gwamnan yankin Luhansk da ke gabashin Ukraine, ya yi gargadin cewa, Rasha na kara zafafa kai hare harenta a yankin, a don haka ya bukaci mutane da su tsere.
Gwamnan ya ce, akwai kusan kaso daya bisa uku na mazauna yankin da suka rage, kuma rayuwarsu na cikin hadari.
Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce yanzu dakarun Rasha sun mayar da hankali ne a gabashi da kudancin kasar wajen kai hare hare.
Mataimakiyar Firaministan kasar, Iryna Vereshchuk, ta ce sojojin Ukraine 12 da fararen hula 14 za su dawo gida a wani bangare na musayar fursunoni.
Ba ta bayyana ko Rashawa nawa aka saka ba.