fidelitybank

Rasha na takalar kungiyar tarayyar Turai fada – EU

Date:

Kungiyar Tarayyar Turai ta ce matakin Rasha na dakatar da sayar wa Poland da Bulgaria gas abu ne da ake kallo da takalar fada da ci da ceto, kamar yadda shugabar hukumar gudanarwar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen ta bayyana.

“Za mu tabbatar matakin da kamfanin Gazprom na Rasha ya dauka, ba zai yi kwakkwaran tasiri ga kasashen Turai da suka dogara da shi ba,” in ji ta a wajen taron manema labarai ranar Laraba.

von der Leyen, ta kuma gargadi kamfanonin makamashin Turai da kasa su amince da sharuddan Rasha na sayan hajarta da kudin kasa Rubble, tare da cewa wannan matakin ya sabawa dokokin takunkuman da da Trayyar Turai ta kakabawa Rasha.

“Biyan kudin gas da Rubble,idan har wasu na ganin ba komai ba ne, to wannan ya sabawa ka’ida kuma yi wa takunkuman da aka sanyawa Rasha hawan kawara ne,” in ji ta.

A karshe ta bayyana cewa kamfanonin da suke mu’amala da Rasha da suke kokarin sayan gas da kudin rubble, su na daukar babbar kasada.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp