Mataimakin magajin garin Mariupol mai tashar jirgin ruwa, wanda dakarun Rasha suka yi wa kawanya ya zargi sojin na Rasha da yin dabaru irin wadanda aka gani a birnin Aleppo na Syria.
Sergei Orlov ya gaya wa BBC cewa, sojojin Rasha na son birnin ya mika wuya domin su jefa jama’a cikin mawuyacin hali.
Ya ce dabarun sun hada da ruwan makamai ta sama ba kakkautawa , da bata gine-gine, wadanda suka hada da makarantu da asibitoci.
Birnin na Mariupol ya shiga kwana na uku ke nan ba wutar lantarki ba ruwa.
A ‘yan mintunan da suka gabata Sakatare janar na NATO, Jens Stoltenberg, ya ce ƙawancen zai karfafa kariyarsa ta kasa da sama da kuma ta ruwa.
Ya ce, wannan shi ne kutsen soji mafi muni a Turai a tsawon gomman shekaru, inda birane ke karkashin mamaya, ake ruwan wuta a kan makarantu, asibitoci da gidajen jama’a.
Sannan ana yin abubuwan da ba su dace ba a kusa da tashar nukiliya a jiya da dare, inda aka kashe farar hula da yawa ko jikkata su.
Fadan da ake gwabzawa kuma ya yadu zuwa wajen wani birnin na kudancin kasar ta Ukraine, Mykolaiv.