fidelitybank

Rasha na salon irin yakin Syria a Ukraine

Date:

Mataimakin magajin garin Mariupol mai tashar jirgin ruwa, wanda dakarun Rasha suka yi wa kawanya ya zargi sojin na Rasha da yin dabaru irin wadanda aka gani a birnin Aleppo na Syria.

Sergei Orlov ya gaya wa BBC cewa, sojojin Rasha na son birnin ya mika wuya domin su jefa jama’a cikin mawuyacin hali.

Ya ce dabarun sun hada da ruwan makamai ta sama ba kakkautawa , da bata gine-gine, wadanda suka hada da makarantu da asibitoci.

Birnin na Mariupol ya shiga kwana na uku ke nan ba wutar lantarki ba ruwa.

A ‘yan mintunan da suka gabata Sakatare janar na NATO, Jens Stoltenberg, ya ce ƙawancen zai karfafa kariyarsa ta kasa da sama da kuma ta ruwa.

Ya ce, wannan shi ne kutsen soji mafi muni a Turai a tsawon gomman shekaru, inda birane ke karkashin mamaya, ake ruwan wuta a kan makarantu, asibitoci da gidajen jama’a.

Sannan ana yin abubuwan da ba su dace ba a kusa da tashar nukiliya a jiya da dare, inda aka kashe farar hula da yawa ko jikkata su.

Fadan da ake gwabzawa kuma ya yadu zuwa wajen wani birnin na kudancin kasar ta Ukraine, Mykolaiv.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp