fidelitybank

Rasha na neman shugaban Ukraine ruwa a jallo

Date:

Kasar Rasha ta sanya shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy cikin jerin sunayen da ake nema ruwa a jallo.

Kamfanin dillancin labaran kasar, TASS ya bayar da rahoton cewa, ma’aikatar harkokin cikin gida ta Rasha ta nuna cewa Zelenskiy na cikin jerin wadanda ake nema ruwa a jallo amma bai bayar da wani karin bayani ba.

Hakan ya faru ne yayin da Rasha ta bude shari’ar laifuka akan Zelenskyy.

Da yake mayar da martani, Ukraine ta yi watsi da rahoton wanda ta bayyana a matsayin shaida na “rashin bege” na Moscow.

Ma’aikatar harkokin wajen Ukraine ta ce shugaban Rasha Vladimir Putin da kansa na fuskantar kame bisa sammacin kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa.

Sanarwar ta ce: “Muna so mu tunatar da ku cewa, ba kamar sanarwar da Rasha ta bayar ba, takardar sammacin da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta bayar na cafke shugaban Rasha Vladimir Putin bisa zarginsa da aikata laifukan yaki gaskiya ne, kuma za a aiwatar da shi a kasashe 123.”

A cewar ma’aikatar, sanarwar ta Rasha ta kasance “shaida ce ta rashin jin daÉ—in na’ura da farfagandar Rasha, wanda ba zai iya tunanin wata hanyar da za ta jawo hankali ba”.

A cikin watan Fabrairun 2022, Rasha ta ba da sammacin kama wasu ‘yan siyasar Ukraine da sauran ‘yan siyasar Turai.

‘Yan sandan Rasha a cikin watan Fabrairu sun sanya Firayim Ministan Estoniya Kaja Kalas, ministan al’adu na Lithuania da ‘yan majalisar dokokin Latvia da ta gabata cikin jerin sunayen da ake nema ruwa a jallo domin rusa abubuwan tarihi na zamanin Soviet.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp