Uwargidan shugaban kasar Ukraine Olena Zelenska ta fitar da wata sanarwa cike da tausayi kan mamayar da Rasha ke yi wa kasarta, tana sukar abin da ta kira “kisan kiyashin” da ake wa fararen hular kasar.
Ta mayar da hankalinta kan ne kan mace-macen kananan yara har ta ambato sunayen was yara uku da suka halaka yayin yakin da ake gwabzawa.
Ta ce Ukraine kasa ce mai nema zaman lumana amam za ta kare ‘yancinta da kan iyakokinta.
Sai dai babu wanda ya san inda Misis Zelenska mai shekara 44 ta ke a halin yanzu, kuma maigidanta Shugaba Zelensky ya ce dakarun Rasha na neman inda iyalansa suke.