Rasha na ci gaba da kai hare-hare biranen Ukraine, wanda tun a daren jiya an yi luguden wuta a babban birnin kasar Kyiv.
Magajin birnin Vitali Klitschko, ya ce, yawancin gidaje da manyan kantunan sayar da kayayyaki sun ragargaje saboda makaman roka da na atilari da sojin Rasha sukai musu.
Tetiana Lomakina ita ce mai bai wa shugaba Zelensky shawara ta ce, al’amari na kara kazanta fiye da yadda ake zato.
Ta ce “Kashi 90 cikin 100 na gine-ginen birnin ya lalace, ba mu san adadin mutanen da baraguzan gini suka danne ba, wanda ba za mu iya cirowa ba, saboda ci gaba da luguden wutar da ake yi mana, ko a jiya bam ya fada wata makarantar yara kananan, abin akwai tada hankali”