Amurka ta ce ta ga alamun da ke nuni da cewa na’urorin tsaron saman Rasha ne suka harbo jirgin saman da ya yi hatsari a Kazakhstan a ranar Laraba .
Kakakin Fadar White House, John Kirby, ya ce Amurka ta yi tayin taimakawa wajen gudanar da bincike kan hatsarin, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutum 38.
Da aka tambaye shi game da zargin, kakakin Kremlin Dmitry Peskov, ya ce Moscow ba ta da abin cewa game da hatsarin.
Ya ce ana gudanar da bincike kan wannan lamarin kuma a halin yanzu ba a kammala ba, don haka babu wani ƙarin bayani da za su bayar da kan hatsarin.